http://s.rfi.fr/media/display/f185e218-4f02-11ea-9c81-005056a964fe/w:1024/p:16x9/2020-02-10t133456z_1407255715_rc2pxe95ajad_rtrmadp_3_china-health_0.jpg
Shugaban China Xi Jinping yayin duba aikin cibiyar dakile yaduwar annobar murar COVID-19 dake yankin Anhuali a Beijing babban birnin China.Xinhua via REUTERS ATTENTION EDITORS

Annobar COVID-19 ka iya tafka barna fiye da 'yan ta'adda - WHO

by

Hukumomin Lafiyar China sun ce an samu karin mutane 121 da annobar murar mashako ta COVID-19 ta halaka a China, kuma 116 daga cikin mamatan sun fito ne daga Lardin Hubei kadai, inda annobar ta samo asali.

Yanzu haka dai annobar cutar ta COVID-19 dake kassara hanyar numfashin dan adam ta halaka jimillar mutane dubu 1 da 488 a kasar ta China.

Kididdigar baya bayan nan da jami’an lafiya a kasar suka fitar kuma ta nuna cewar, mutane dubu 51 da 986 ne suka kamu da murar mashakon ta COVID-19 a Lardin Hubei kadai, tun bayan bullarta a Wuhan babban birnin lardin.

A fadin kasarta China kuwa sabuwar kididdigar ta ce kusan mutane dubu 65 annobar ta shafa, bayan gano karin mutane dubu 5 da 90 da suka kamu.

Kawo yanzu dai annobar murar ta COVID-19 ta bazu zuwa akalla kasashe 25, inda ta halaka mutane 3, a Hong Kong, Philippines da kuma Japan.

A baya bayan nan shugaban hukumar lafiya ta duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus yayi gargadin cewar, cutar ka iya tafka barna sama da ayyukan ‘yan ta’adda.